Category: labarai

  • Gwamnatin kano ta ce ba za tayi watsi da matasan da suka tuba ba

    Gwamnatin kano ta ce ba za tayi watsi da matasan da suka tuba ba

    Gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusif ta bayyana cewa ba za ta yi watsi da matasan da suka tuba daga harkar fadace fadacen daba ba, domin kuwa suna da baiwar da suke da ita wacce za ta amfanar da al’umma muddin aka basu kulawar da ta dace.

    Kwamishinan Yaɗa labarai da harkokin cikin gida na jihar, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ne ya bayyana hakan a yayin wani taron da aka shirya domin karɓar wasu daga cikin matasan da suka yanke shawarar barin harkar daba.

    Kwamishinan ya bayyana cewa zuwa yanzu an tantance matasa sama da dubu 1 da 600 da aka saka cikin shirin Safe Corridor, kuma nan gaba kadan za’a ci gaba da tantance wasu matasa 2,100 domin su ma su shiga cikin shirin.

    Haka kuma ya ce bayan kammala wannan mataki za a mika su gaban gwamna domin karɓar tallafin da zai basu na dogaro da kansu.

    Waiya ya tabbatar da cewa gwamnatin kano za ta ci gaba da tallafawa matasan da suka nuna dabi’u masu kyau wajan samun ingantacciyar rayuwa.

    Da yake nasa jawabin a madadin maimartaba sarkin Kano Dan Amar din Kano Alhaji Aliyu Harazimi ya bukaci Matasan da su dage wajen komawa ga Allah, domin hakan yana kawar da mutane daga aikata abubun da basu dace ba

    wannan shine karo na uku da kwamishin na yada labarai da harkokin cikin gida na kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya jagoranci zaman tattaunawa da kwamitin zaman lafiya na safe Corridor domin cigaba da tattance su da kuma samar da hanyoyin cika musu alkawarin da gwamnatin kano ta dauka a kansu.

  • Karota ta yi alƙawarin mika buƙatun ɗaliban Jami’ar Sule Lamido ga hukumomin da suka dace

    Karota ta yi alƙawarin mika buƙatun ɗaliban Jami’ar Sule Lamido ga hukumomin da suka dace

    Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Jihar kano (KAROTA) tayi alkawarin mika bukatun daliban Jami’ar Sule Lamido dake Kafin Hausa, a Jihar Jigawa, ‘yan asalin Jihar Kano, domin magance musu matsalolin sufuri daga Kano zuwa Jihar Jigawa.

    Shugaban hukumar KAROTA, Hon. Faisal Mahmud Kabir, ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi baƙuncin ƙungiyar daliban Jami’ar Sule Lamido dake Kafin Hausa, a makon da ya gabata.

    Cikin wata sanarwa da Jami’in Yaɗa Labarai na Hukumar, Abubakar Ibrahim Sharada, ya fitar a yau Lahadi, 2 ga watan Nuwamba 2025.

    shugaban hukumar ya kuma bukaci daliban da su kasance jakadu na gari, waɗanda Jihar Kano za ta yi alfahari da su a nan gaba.

    Hon. Faisal ya ƙara da cewa, hukumar za ta tuntubi ma’aikatar Aiyuka domin samar musu da dakunan kwana ga daliban Jihar Kano sama da 4,000, domin rage musu kuɗin masauki, Da kuma tallafa musu wajen samun ilimi cikin sauƙi.

    A nasa jawabin, shugaban ƙungiyar daliban Jami’ar Sule Lamido dake Kafin Hausa, Comrade Habibu Abdullahi Abubakar, ya bayyana cewa sun kai wannan ziyara ne domin miƙa buƙatun ƙungiyar, tare da ƙara ƙarfafa alaƙar haɗin gwiwa tsakanin daliban da hukumar KAROTA.

    A ƙarshe, shugaban hukumar KAROTA, Hon. Faisal Mahmud Kabir, ya gode wa daliban bisa wannan ziyara da suka kawo masa, tare da bayar da tabbacin cewa hukumar za ta ci gaba da tallafa musu duk lokacin da buƙatar hakan ta taso.

  • Sojoji Sun kai samame a ƙaramar hukumar Shanono dake jihar Kano

    Sojoji Sun kai samame a ƙaramar hukumar Shanono dake jihar Kano

    Dakarun sojin ƙasar nan sun kai samame a yankin Faruruwa, kusa da kauyukan Goron Dutse da Tsaure a ƙaramar hukumar Shanono, a daren Asabar, inda suka halaka ‘yan bindiga da dama tare da kama wasu.

    A yayin sumamen sojojin sun kwato babura kusan 30 da ake amfani da su wajen kai hare-hare a yankunan karkara.

    Samamen ya kasance na ci gaba da yaki da ‘yan bindiga a arewacin Kano, wanda ya haɗa da sintiri da kuma fatattakar yan Ta’adan da ke ɓoye a dazuzzuka.

    Sai dai a yayin arangamar, sojojin sun yi rashi, inda aka tabbatar da mutuwar soja ɗaya.

    Nasarar sojojin na zuwa ne bayan da suka sami rahoton afkawar ƴan bindigar wasu ƙauyukan yankin inda suka yi yunƙurin tafiya da ɗaruruwan dabbbobi sai dai sojojin sun rutsasu inda sukai masu fata fata.

    Shugaban ƙaramar hukumar Shanono Hon. Abubakar Barau ya yaba da namijinƙoƙarin jamian tsaron tare da yin alƙawarin cigaba da basu dukkan irin gudummawar da suke buƙata ta kowacce fuska.

    Shaugaban ƙaramar hukumar ta Shanono ya godewa gwamnatin jiha data tarayya bisa yadda take ƙoƙari babu dare ba rana domin ganin an kakkaɓe ƴan bindigar dake kutsawa yankin na Shanono.

    Tuni dai aka tura ƙarin dakarun ƙasa da na sama domin ci gaba da aiki a yankin da kewaye, da nufin tabbatar da cewa ba a bai wa ‘yan bindigar damar sake komawa ba.