labarai

Da ɗumi-ɗumi: Gwamna Abba Kabir Yusuf zai koma APC ranar Litinin

Rahotanni daga DAILY NIGERIAN sun tabbatar da cewa Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, zai sauya sheƙa daga jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a hukumance ranar Litinin mai zuwa.

Majiyoyi masu tushe sun bayyana cewa gwamnan ya riga ya isa Abuja domin kammala shirye-shiryen ficewarsa daga NNPP.

Rahoton ya ce Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, tare da shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Yitwalda Nentawe, ne za su karɓi gwamnan a birnin tarayya.

Haka kuma, an tabbatar da cewa jagoran APC a Kano, Abdullahi Ganduje, an kira shi da gaggawa daga tafiyar da yake yi a Dubai.

A gefe guda kuma, shugaban APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas, ya rage zamansa a Umrah domin shirya ba gwamnan katin zama ɗan APC a Diso Ward, Karamar Hukumar Gwale a cikin makon nan.

Idan hakan ta tabbata, Abba Kabir Yusuf zai zama gwamnan NNPP na ƙarshe da ya bar jam’iyyar, lamarin da ke ƙara ɗaga kura a fagen siyasar Kano da Arewa baki ɗaya.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button